An harbe mutanen ne a lokacin da 'yan sandan farin kaya suka farwa maboyarsu dake yankin Bali na jihar a daren ranar Laraba.
Kwamishinan 'yan sandan jihar, David Akinremi, ya shaidawa manema labarai a birnin Jalingo cewa, masu satar mutanen da aka kashe sun addabi jama'ar yankin Bali dake lardin Takum na jihar.
David Akinremi, ya kara da cewa, masu satar mutanen sun sace mutane da dama, inda suke amfani da wani sansani a kauyen Garuwa a matsyin inda suke ajiye su.
Ko a karshen watan Maris din da ya gabata, 'yan sanda sun kashe wasu mutane 5 da ake zargin masu satar mutane ne don neman kudin fansa, a dai wannan yanki na jihar Taraba, biyo bayan samamen da suka kai maboyarsu.
A watan Junairun da ya gabata ne aka sace wani dan majalisar dokokin jihar a yankin Takum, inda daga bisani bayan kwanaki, aka tsinci gawarsa. (Fa'iza Mustapha)