in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Najeriya sun hallaka mayakan Boko Haram 23
2018-06-13 20:15:43 cri
Rundunar sojojin Najeriya dake aikin sintiri a yankin tafkin Chadi, ta ce dakarun ta sun hallaka mayakan Boko Haram 23, yayin wani samame da suka gudanar a wasu maboyar 'yan ta'addan.

Da yake tabbatar da hakan ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Larabar nan, kakakin rundunar Texas Chukwu, ya ce da yawa daga 'yan ta'addan sun tsere da raunukan bindiga, bayan dauki ba dadi da sassan biyu suka gwaza da yammacin ranar Litinin.

Chukwu ya ce dakarun Najeriyar sun gudanar da aiki ne a yankin da hadin gwiwar kasar Kamaru. Kaza lika dakarun sojin sun gano tarin harsasai da mayakan Boko Haram ke amfani da su.

A ranar 15 ga watan Mayu ne dai Sojojin Najeriyar suka kaddamar da wani aikin soji na watanni 4, a wani mataki na kakkabe gyauron mayakan na Boko Haram daga dukkanin yankunan tabkin Chadi.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China