in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta taimaka ga karfafa hadin-gwiwa tsakanin kasashe membobin kungiyar SCO
2018-06-11 20:54:39 cri
Mai magana da yawu ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Geng Shuang, ya bayyana a yau Litinin cewa, kasarsa za ta yi kokari tare da sauran kasashe membobin kungiyar hadin-kai ta Shanghai ko kuma SCO a takaice, domin tabbatar da nasarorin da aka samu a wajen taron kolin da aka gudanar a kwanan baya a birnin Qingdao, da kara fadada hadin-gwiwa tsakaninsu, ta yadda za su samu makoma mai haske.

A 'yan kwanakin baya ne dai aka rufe taron kolin kungiyar SCO a birnin Qingdao. Yayin da yake amsa tambayoyi game da taron, Mista Geng ya jaddada cewa, taron ya saka wasu sabbin abubuwan zamani a cikin Ruhin Shanghai, da kuma kafa sabon burin da kungiyar SCO ke kokarin cimmawa, gami da sabuwar alkibla ga hadin-gwiwar kasashe membobin kungiyar.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China