in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta nace wa hanyar ci gaba ba tare da barazana ga kowa ba, in ji Yu Jianhua
2018-06-06 09:49:47 cri

Jakadan kasar Sin a ofishin MDD dake birnin Geneva Yu Jianhua ya ce, ci gaban kasar Sin tamkar ci gaban duniya ne baki daya, duba da yadda hakan ke tallafawa zaman lafiya da bunkasar duniya, tare da daga matsayin huldar kasa da kasa.

Yu Jianhua, ya bayyana hakan ne a yayin taron kara wa juna sani da ya gudana a ranar Talata, yana mai cewa duk irin ci gaba da Sin za ta samu, ba zai zamo barazana ga sauran kasashen duniya ba, kana hakan ba zai zamo yunkuri na wargaza yanayin da duniya ke ciki, ko wani yunkuri na samarwa kai tasiri kan wasu ba.

Jami'in ya kara da cewa, "Kasar Sin mai karfin ci gaba za ta haifar da wanzar da zaman lafiya da lumana". Ya ce, duk da ci gaban da Sin ta samu cikin 'yan shekarun baya-bayan, babban burin kasar shi ne fadada bunkasuwar ta a dukkanin fannoni.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China