in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman kasar Sin: Kamata ya yi Palasdinu da Isra'ila su maido da shawarwari tsakaninsu
2018-06-01 10:49:18 cri
Manzon musamman mai kula da batun yankin gabas ta tsakiya Mista Gong Xiaosheng wanda ya kai ziyara a kasasr Masar ya bayyana a jiya 31 cewa, kamata ya yi Palasdinu da Isra'ila su dakatar da bude wuta a tsakaninsu, hanya daya tilo da za su bi wajen warware rikici ita ce yin shawarwari a siyasance.

A yayin wani taron manema labarai da aka yi a wannan rana, Gong Xiaosheng ya ce, babban burin ziyarar tasa a wannan karo a Palasdinu, Isra'ila da Masar shi ne yin musanyar ra'ayi da bangarori masu ruwa da tsaki kan halin dake kara tsananta tsakanin Palasdinu da Isra'ila da dai sauran manyan matsaloli a wannan yanki.

Bangarori mahalarta taro su ma sun yi maraba da sabuwar gudunmawa da Sin take bayarwa wajen wanzar da zaman lafiya a yankin.

Gong Xiaosheng ya ce, Sin na nacewa ga warware rikicin banganrorin biyu ta hanyar yin shawarwari cikin lumana, kuma Sin na fatan kara ba da gudunmawa na ganin an wanzar da zaman lafiya a yankin, don kwantar da hankali da tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Kasar Sin na ganin cewa, ya kamata kasashen duniya su nace ga manufar kafa kasashe biyu, su kuma ba da gudunmawa don warware wannan rikici a siyasance bisa kudurin MDD da yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya a kasashen Labarawa da sauran matsaya daya da aka cimma. (Amina Xu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China