in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan Amurka da Koriya ta Arewa za su ci gaba da daidaita sabaninsu ta hanyar yin shawarwari
2018-05-25 18:51:17 cri
Game da sabbin maganganun da shugabannin kasashen Amurka da Koriya ta Arewa suka yi dangane da ganawarsu, mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lu Kang ya ce, ganawar shugabannin biyu za ta taimaka matuka ga yunkurin kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya, kuma Sin na fatan bangarorin biyu za su ci gaba da yin shawarwari don warware batutuwan dake jawo hankalinsu, da sa kaimi ga ci gaban yunkurin kauda makaman nukiliya a zirin.

Jiya Alhamis, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar da soke shawarwarin da zai yi da takwaransa na Koriya ta Arewa a ranar 12 ga watan Yulin bana a kasar Singapore. A jiya ne kuma, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Koriya ta Arewa, Kim Kye-gwan ya bayyana cewa, kasarsa na son komawa teburin shawarwari da kasar Amurka a kowa ne lokaci kuma ta hanyar da ta dace.

Game da wannan batu, Lu Kang ya ce, kasar Sin na fatan bangarorin biyu za su kara nuna juriya da hada kai tare, don ci gaba da warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari.

Har wa yau, Lu ya ce, kasar Sin na maraba da matakin da Koriya ta Arewa ta dauka, na lalata cibiyar gwajin makaman nukiliya na Punggye-ri.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China