in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IAEA: Iran tana bin yarjejeniyar nukiliya yadda ya kamata
2018-05-10 10:15:22 cri
Babban jami'in hukumar makamashin nukiliya ta kasa da kasa IAEA Yukiya Amano, ya fidda wata sawarwa a jiya 9 ga wata, wadda ke cewa, IAEA na da tabbacin game da yadda Iran ke yin biyayya ga yarjejeniyar nukiliyar ta yadda ya kamata, kuma hukumar za ta ci gaba da mai da hankali kan lamarin dake da nasaba da yarjejeniyar.

A cikin wannan sanarwa, Yukiya Amano ya bayyana cewa, bisa yarjejeniyar nukiliyar Iran da aka cimma tsakanin bangarorin daban-daban a watan Yuli na shekarar 2015, Iran tana karkashin cikakken bincike daga IAEA.

A watan Yuli na shekarar 2015, Iran da kasashe shida wato Amurka, Birtaniya, Faransa, Rasha, Sin da Jamus, sun kai ga cimma matsaya daya kan yarjejeniyar nukiliyar Iran.

Bisa wannan yarjejeniya, Iran ta yi alkawarin kayyade shirin ta na makaman nukiliya, tare da amfani da makamashin nukiliyar yadda ya kamata. Hakan ya sa kasashen duniya suka janye takunkumin da suka kakkabawa Iran din.

To sai dai kuma shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar a ran 8 ga wata cewa, Amurka za ta janye daga wannan yarjejeniya, tare da maido da takunkumi kan Iran. (Amina Xu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China