in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rahoton MDD: Sauyin tsarin tattalin arzikin kasar Sin zai haifar da babban tasiri ga tattalin arzikin yankin Asiya da tekun Pasifik
2018-05-08 10:24:49 cri
Kwamitin kula da tattalin arzikin yankin Asiya da tekun Pasifik na MDD da ke da hedkwata a birnin Bankok na kasar Thailand, ya ce sauyin tsarin tattalin arzikin kasar Sin zai haifar da muhimmin tasiri ga sauran kasashen yankin Asiya da tekun Pasifik ta fannonin ciniki da zuba jari.

Rahoton da kwamitin ya fitar a jiya mai taken, "hasashen harkokin tattalin arziki da zaman al'umman Asiya da tekun Pasifik a shekarar 2018", ya yi nuni da cewa, bunkasuwar kasuwannin cikin gida a kasar Sin za ta samar da zarafi ga abokan cinikinta da ke yankin, yayin da yadda kasar ke kara zuba jari ga kasashen waje, zai taimaka wajen kulla huldar samun moriyar juna da abokan cinikanta.

A wurin taron kaddamar da rahoton, Hamza Ali Malik, jami'in sashen kula da manufofin tattalin arziki da tara jari na kwamitin ya bayyana cewa, kasar Sin na kan gaba a fannin hada-hadar kudi da fasahohi na duniya, kuma kwarewar kasar ta fannin kirkire-kirkire na haifar da tasiri ga sauran kasashen shiyyar. Yana mai cewa, fasahohin da kasar ke da su sun cancanci a yi nazari kansu.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China