Ministan harkokin waje na kasar Sin ya jinjinawa ganawar sassan koriya ta kuda da ta arewa
Dan majalissar zartaswar kasar Sin, kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya jinjinawa ganawar da shugabannin koriya ka kudu da ta arewa suka yi a watan da ya gabata, yana mai cewa hakan ya haifar da babbar gajiya, da damammaki na warware sa-in-sa da ake fama da shi game da batun zirin koriya.
Mr. Wang Yi wanda ke ziyarar aiki a koriya ta arewa a Alhamis din nan, ya yi tsokacin ne yayin ganawarsa da shugaban kasar Kim Jong Un.