in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran ta yi watsi da zargin da Morocco ta yi mata na goyon bayan 'yan aware
2018-05-02 19:35:43 cri
Ma'aikatar harkokin wajen Iran, ta ce babu kamshin gaskiya game da zargin da kasar Morocco ta yi, na cewa Iran din na tallafawa kungiyar 'yan aware ta Polisario dake yammacin Sahara mai adawa da gwamnatin Morocco.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Iran Bahram Qasemi, ya ce wancan zargi na Morocco ba shi da tushe bare makama. Kuma Iran ba ta taba shiga sabgar wata kasa ta daban ba.

A ranar Talata ne dai Morocco ta ce za ta yanke huldar diflomasiyya da Iran. A cewar Firaministan kasar Morocco Nasser Bourita, kasar sa za ta kori jakadan Iran daga birnin Rabat, za kuma ta rufe ofishin ta na jakadanci dake birnin Tehran.

Ministan harkokin wajen Moroccon ya kara da cewa, kasar sa tana da kwararan shaidu, dake nuna cewa, Iran ta hannun kawar ta wato kungiyar Hezbollah dake kasar Lebanon, na taimakawa kungiyar Polisario da kudade, da samar da horo, domin kungiyar ta iya kaiwa ga gurgunta tsaro da zaman lafiya a Morocco.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China