in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta fitar da dokokin bude bangaren sayar da takardun hada-hadar kudi ga baki masu sha'awar zuba jari
2018-04-29 16:56:03 cri
Hukumar kula da takardun hada-hadar kudi ta kasar Sin(CSRC) ta fitar da wasu sabbin dokoki game da zuba jarin waje a bangaren takardun hada-hadar kudin kasar, a wani mataki da gwamnati ta dauka na kara bude kofa a bangaren kudaden kasar.

Gwamnan babban bankin kasar Sin Yi Gang wanda ya sanar da hakan yayin taron manema labarai, ya ce dokokin hukumar da aka yiwa gyaran fuska za su baiwa masu sha'awar zuba jari na kasashen ketare damar mallakar kamfanoni kasuwar hannayen jari na hadin gwiwa, tare da alkawarin fadada hada-hadar irin wadannan kamfanoni.

Ya ce, an dauki wadannan matakai ne kamar yadda hukumomi suka sanar a dandalin shekara-shekara na Asiya na Boao da ya gudana a farkon wannan wata. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China