in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta karfafa hadin kai da Tarayyar Afirka ta fuskar tsaro da zaman lafiya
2018-04-23 11:08:30 cri
Jakadan kasar Sin a Tarayyar Afrika Kuang Weilin, ya ce kasar Sin za ta kara karfafa hadin gwiwa da Tarayyar Afrika AU, ta fuskar tsaro da tabbatar da zaman lafiya.

Da yake ganawa da Xinhua, Jakadan ya ce zaman lafiya da tsaro babban bangare ne da kasar Sin da AU da kuma kasashen Afrika ke hadin gwiwa, inda kasar Sin ke taimakawa da dakaru da kuma shirye shiryen horo.

Jami'in na magana ne a karshen taron manyan jami'ai da aka yi kan tsaro a nahiyar a Afrika, wanda ya gudana a birnin Bahir Dar na arewacin Habasha daga ranar 21 zuwa 22 ga watan nan.

Kuang Weilin ya ce a yanzu, kasar Sin na aiki kafada da kafada da AU, domin cika alkawarin nan na 2015, dake da nufin samar da tallafin dala miliyan 100 ga Rundunar ko-ta-kwana ta Afrika wato ASF.

Ya ce idan babu zaman lafiya da tsaro, to ba za a samu ci gaba ba, a don haka, za su yi duk abun da za su iya wajen bada gudunmuwa ga zaman lafiya da tsaro a nahiyar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China