A gun bukukuwa masu gabatar da fina-finai na bikin fina-finai na kasa da kasa na Beijing da aka yi a yau Laraba 18 ga wata, mataimakin shugaban hukuma mai kula da yada labarai, radio da telabijin da sha'anin dab'i ta kasar Sin Mista Hu Dong ya shedawa manema labarai cewa, a cikin shekaru 2 ko 3 masu zuwa, birnin Beijing zai kara saurin kafa gidajen kallo na Sinima a wasu karkara don jama'a su samu karin damammakin kallon fina finai ba tare da sun yi tafiya zuwa wurare masu nisa ba.
Bisa shirin da aka tsara, yawan Sinima zai kai 300 nan da shekarar 2020, a waccan lokaci kuma jama'a zasu kalli fina finai cikin sauki. (Amina Xu)