in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya bukaci yankunan raya tattalin arziki na musamman su kasance kofar samar da sauye sauye da kara bude kofa
2018-04-13 20:56:07 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping na fatan gina lardin Hainan ta yadda zai zama wani yankin gwaji na gudanar da cinikayya maras shingeya, ya kuma bukaci yankunan raya tattalin arziki na musamman, su kasance kofar samar da sauye sauye da kara bude kofa ga kasashen waje.

Shugaba Xi, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin na koli na JKS, kuma shugaban kwamitin koli na sojin kasar Sin, ya bayyana hakan ne a juma'ar nan, a jawabin da ya gabatar na bikin cikar lardin na Hainan, da yankin tattalin arziki na musamman na Hainan shekaru 30 da kafuwa.

Ya ce ya kamata yankunan raya tattalin arziki na musamman, su kasance kan manufar da aka kafa su, tare da amfani da matsayin da aka ba su, domin cimma burin da aka sanya gaba. Kaza lika shugaban na Sin ya bukace su da su ci gaba da zama mafari na aiwatar da sauye sauye, da kara bude kofa ga ketare.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China