Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da tsoffi da sabbin mambobin kwamitin dandalin Boao a yau Laraba a garin Boao na lardin Hainan.
Yayin ganawar, Mista Xi ya jaddada cewa, muhimmin sakon da Sin take samu wajen aiwatar da manufar bude kofa ga kasashen waje da yin gyare-gyare a gida a cikin shekaru 40 da suka gabata shi ne: ci gaban kasar Sin da na duniya sun dogara da juna. Ya ce Sin za ta ci gaba da nacewa ga samun ci gaba cikin lumana, da aiwatar da manyan satre-tsare na bude kofa ga kasashen waje domin samun moriyar juna da nasara tare, tare kuma da sa kaimi ga samar da wani yanayi na mutunta juna, mai adalci da tabbatar da daidaito da kuma kawo moriya ga juna a tsakanin kasa da kasa. (Amina Xu)