in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ba ta tsoron matakai mara kan gado da gwamnatin Trump za ta dauka kanta ba
2018-04-07 17:54:20 cri
Gwamnatin Amurka a Jiya Jumma'a, ta ce tana tunanin kara haraji kan kayayyakin da darajarsu ta kai dala biliyan 100 da Sin ke shigarwa kasarta, lamarin da ya haddasa raguwar darajar hannayen jari a kasuwannin Amurka matuka, baya ga haddasa damuwa ga masu zuba jarin.

Bayan Donald Trump ya hau kan ragamar mulkin Amurka, ya fara nuna kiyaya ga kasa da kasa, kamar bincike mai lamba 232 da ma'aikatar kasuwancin kasar ta yi kan kayayyakin karafa da na gorar ruwa da ake shigar da su kasarsa daga ketare, sa'an nan, ya kuma bukaci yin gyare-gyare kan yarjejeniyoyin ciniki da kasarsa ta riga ta kulla da kawayenta. Zuwa yanzu kuma, ya yi bincike bisa doka mai lamba 301 domin cin zarafin kasar Sin. Amma kasar Sin ta nuna aniyarta ta mai da martani kan dukkan matakai mara kan gado da Amurka za ta dauka a kanta. Kasar Sin ta bayyana cewa, idan gwamnatin Amurka karkashin Donald Trump tana son ci gaba da wannan harka, to ita ma ba za ta ji tsoro ba, kuma tabbas za ta mai da martani daidai da na Amurka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China