in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahukuntan Najeriya sun tabbatar da sakin wasu daga 'yan matan Dapchi
2018-03-21 19:26:50 cri
Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da sakin wasu daga 'yan matan sakandaren garin Dapchi na jihar Yobe su 110 da kungiyar Boko Haram ta sace a kwanakin baya.

Mai magana da yawun fadar shugaban Najeriyar Garba Shehu, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua hakan ta wayar tarho, yana mai cewa yanzu haka an debe 'yan makarantar da suka samu kubuta zuwa wani killataccen wuri domin kula da su.

Garba shehu ya ce yana da tabbacin an saki 'yan matan, sai dai ba shi da yakini game da takamaiman yawan su a daidai lokacin zantawar tasa da Xinhua. Ya ce ba a kai ga samun cikakkun bayanai ba tukuna.

Mazauna yankin na Dapchi sun bayyana cewa, wasu mutane da suke zaton mayakan kungiyar Boko Haram ne suka dawo da 'yan matan cikin wasu manyan motoci, irin wadanda aka yi amfini da su wajen kwashe su daga makarantar tasu a ranar 19 ga watan Fabarairun da ya shude.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China