in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ja hankalin kasashen Afirka game da daukar matakan cimma nasarar shirin AfCFTA
2018-03-19 20:20:58 cri
Jami'an MDD da na kungiyar hadin kan Afirka ta AU, sun ja hankalin kasashen nahiyar Afirka, game da bukatar daukar sahihan matakai, na cimma nasarar kafa yankin ciniki cikin 'yanci na nahiyar ko AfCFTA a takaice.

Da take tsokaci game da hakan, shugabar hukumar zartaswar AU kuma ministar harkokin wajen kasar Rwanda Louise Mushikiwabo, ta ce ya kamata kasashen nahiyar su lura da cewa su ne za su tabbatar da yadda yankin ciniki cikin 'yanci na nahiyar zai kasance. Ta na mai cewa dukkanin kasashen nahiyar na da rawar takawa don ganin an cimma nasara.

Ministar wadda ke wannan tsokaci a birnin Kigalin kasar Rwanda, ta ce ya zama wajibi kasashen Afirka, su tunkari kalubalen dake gaban su, wanda suka hada da na dokoki, da na samar da kudade daga sassa masu zaman kan su, da na ababen more rayuwa, da batun ayyukan lura da shige da fice, muddin dai suna fatan ganin ci gaba a fannin bunkasar cinikayya tsakanin su.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China