in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ta saurari daftarin dokar sa ido da shirin sake fasalin ma'aikatu
2018-03-14 10:49:21 cri
Majalisar wakilan jama'ar kasar Sin(NPC) ta saurari daftarin dokar sa ido da na shirin sake fasalin ma'aikatun majalisar gudanarwar kasar yayin zamanta na jiya.

Zaman na hudu na zagaye na farko na taron majalisar NPC karo na 13 da ya gudana a jiya, ya samu halartar Shugabannin kasar Sin da suka hada da Xi Jinping da Li Keqiang da sauransu.

Wakilan jama'ar sun amince da samar da kwamitoci na musammam ga majalisar ta 13, tare da zabar shugabanni da mataimakansu da kuma mambobi.

Bisa matakin da suka dauka, majalisar karo na 13 za ta kunshi kwamitocin musammam guda 10, wadanda za su mayar da hankali kan bangarorin da suka shafi harkokin kabilu da na kundin tsarin mulki da dokoki da harkokin kasashen waje da kare muhalli da harkokin noma da kuma na karkara.

Yayin taron na jiya, wakilan sun amince da jerin sunayen shugabanni da mataimakansu da kuma mambobin kwamitin kula da dokoki da kundin tsarin mulki da na kwamitin kula da harkokin kudi da tattalin arziki. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China