in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai wani harin ta'addanci a Burkina Faso
2018-03-02 20:29:03 cri
Rahotanni daga Ouagadougou,babban birnin kasar Burkina-Faso na cewa, an ji karar bindigogi da wasu abubuwan fashewa a hedkwatar soja da ba ta da nisa da babbar kasuwar birnin.

Majiyoyi na cewa, kura na tashi sama sakamakon abubuwan da suka fashe. Haka kuma an ji karar harhe-harbe a kusa da ofsihin jakadancin kasar Faransa dake birnin Ouagadougou. Jama'a dai na arcewa ta ko'ina don neman tsira da rayukansu.

Rundunar 'yan sandan Burkina Faso ta tabbatar da cewa, hari ne na ta'addanci, kuma an killace wurin da aka kai wannan hari. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China