in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan za a cimma daidaito dangane da yiwa kwamitin sulhun MDD kwaskwarima
2018-02-03 17:32:16 cri
A ranar 1 ga watan nan na Fabrairu, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya halarci taron shawarwari karo na farko dangane da yiwa kwamitin sulhun MDD kwaskwarima wanda aka gudanar a yayin babban taron MDD karo na 72 a hedkwatar majalisar dake birnin New York.

A wajen taron, Mr. Ma Zhaoxu, ya yi nuni da cewa, a cikin shekaru sama da 70 da kafa MDDr, mambobinta sun karu daga 51 zuwa 193, kuma akasarinsu kasashe masu tasowa ne, a yayin da kasashen Afirka suka zarce rubu'i na baki dayan mambobin. A halin da ake ciki yanzu, kasashe masu tasowa da ma kasashen Afirka suna kara tasirinsu, don haka, ya kamata a kara musu wakilci a yayin da ake yiwa MDD kwaskwarima, ta yadda zasu iya kara bayyana ra'ayoyinsu a yayin da kwamitin sulhu ke tsaida duk wani kuduri.

Mr. Ma Zhaoxu ya ce, kullum kasar Sin na goyon bayan yiwa kwamitin sulhu gyare-gyaren da suka dace, kuma tana son hada kan sassa daban daban na duniya, don gudanar da wannan aiki bisa ga moriyar bai daya ta illahirin mambobinta da kuma samar da kyakkyawar makoma ga MDDr.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China