in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ceto masu aikin hakar ma'adanai sama da 900 a Afrika ta kudu
2018-02-03 13:49:37 cri
An samu nasarar ceto ma'aikatan hakar ma'adanai sama da 900 wadanda suka makale a karkashin kasa bayan da aka samu tangardar katsewar lantarki a yayin da suke aikin hakar zinare a jahar Northern Free ta kasar Afrika ta kudu a ranar Juma'a.

An tabbatar da cewa, lamarin ya faru ne sakamakon mamakon ruwan sama da aka samu a daren ranar Laraba, lamarin da ya haifar da katsewar layukan wutar lantarki, inda aka samu mummunan daukewar wutar lantarki, lamarin da ya sa na'urar dake dauko ma'aikatan daga karkashin kasa ta kasa yin aiki.

A cewar kakakin kamfanin Sibanye-Stillwater da ke gudanar da wannan mahakar zinari, wannan wani yanayi ne da ba'a saba ganin irinsa ba. Sai dai yace a nazarci yadda lamarin ya faru domin daukar matakan da suka dace.

An rawaito cewa kamfanin yayi amfani da injinan samar da lantarki don ceto ma'aikatan. A cewar rahotannin farko da aka fitar, injinoyin dake aiki sun fuskanci tangardar manhajar na'ura mai kwakwalwa a lokacin da suke fadi-tashin ceto ma'aikatan.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China