Nasarar da Super Eagles din ta samu a wasan na yammacin jiya Laraba wanda aka buga a birnin Marrakech na kasar Morocco, ya ba ta damar kaiwa wasan karshe na wannan gasa.
A ranar Lahadi ne kuma kungiyar za ta buga wasan karshe da takwararta, kuma mai masaukin bakin gasar wato kasar Morocco, wadda tuni ta lallasa Libiya da ci 3 da 1 a wasan kusa da na karshe da suka buga.