in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta aike da tawaga mai mutane 82 zuwa gasar Olympics ta PyeongChang
2018-01-31 19:51:01 cri
Kasar Sin ta aike da tawagar 'yan wasa 82 zuwa gasar Olympics ta lokacin hunturu ta bana, wadda za a gudanar a birnin PyeongChang na koriya ta kudu.

Da yake tabbatar da hakan a Larabar nan, mataimakin jagoran tawagar Yang Shu'an, ya ce 'yan wasan Sin za su shiga gasanni 55 a rukunoni 12 da za a fafata.

A makamanciyar wannan gasa da ta gabata a birnin Sochi na kasar Rasha, Sin ta samu lambobin zinari 3, da na azurfa 4, da kuma na tagulla 2, wanda hakan ya sanya ta kasancewa kasa ta 12 a kasashe mafiya lashe lambobin zinari a gasar.

Gasar ta 2018 dai za a bude ta ne a ranar 9 ga watan Fabarairu, kuma za a fafata a gasanni 15.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China