in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: A bara sama da mutane miliyan 5.5 sun rasa matsugunnan su a yankin kahon Afirka
2018-01-30 21:11:50 cri
Ofishin MDD mai lura da tsare tsaren ayyukan jin kai ko OCHA a takaice, ya ce ya zuwa karshen watan Disambar bara, sama da mutane miliyan 5.5 ne suka rasa matsugunnan su a yankunan kahon Afirka, ciki hadda kimanin mutum miliyan 4.1 da ke gudun hijira cikin kasashen su, da kuma wasu miliyan 1.4 dake neman mafaka a kasashen da ba na su ba.

Wani rahoto da ofishin OCHA ya fitar a Talatar nan, ya bayyana yankin kahon Afirka a matsayin muhimmin zango na 'yan gudun hijira da bakin haure, wadanda ke zirga zirga zuwa zirin kasashen larabawa da na Turai.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China