in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar wakilan jama'ar kasar Sin za ta yi zaman ta a ranar 5 ga watan Maris
2018-01-30 20:42:52 cri
Majalisar wakilan jama'a ta kasar Sin za ta yi zaman ta na shekara shekara a ranar 5 ga watan Maris, domin tattauna batun yi wa tsarin mulkin kasar kwarkwarima tare da zaben shugabannin yankuna.

Hakan dai na kunshe ne cikin kudurin da majalissar ta cimma yayin taron zaunannen kwamitinta da ya gudana a Talatar nan. An cimma matsaya game da hakan ne bayan kada kuri'u tsakanin mambobin zaunannen kwamitin majalissar a ranekun litinin da kuma Talatar nan.

Majalisar wakilan jama'a ta kasar Sin ko NPC a takaice, ita ce majalissa mafi girma bisa kundin tsarin mulkin kasar Sin, wadda a karkashin ta al'ummar kasar ke kare ikon su na gudanar da harkokin kasar. Ana kuma zaben wakilan ta bisa wa'adi na shekaru biyar biyar, kana zaunannen kwamitin majalisar ya kan kira taron shekara shekara na majalisar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China