in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahalarta taron Davos sun nuna yabo ga manufofin tattalin arziki na kasar Sin
2018-01-25 10:37:13 cri
A ranar 23 ga wata, mamban hukumar siyasa ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, wanda kuma shi ne darektan ofishin kula da harkokin kudi da tattalin arziki na gwamnatin kasar Sin Liu He, ya halarci taron shekara shekara na dandalin tattaunawar tattalin arzikin duniya karo na 48, inda kuma ya gabatar da jawabi, jawabin kuma da ya samu yabo daga mahalarta taron.

Mai taimakawa ministan kula da harkokin waje da hadin gwiwa da kasa da kasa na hadaddiyar daular Larabawa Mohammed Sharaf ya ce, manufar kasar Sin ta bude kofa ga kasashen waje, ba kawai tana taimakawa ga bunkasuwar kasar Sin ba ne, har ma tana amfanar duniya baki daya.

A game da matsalar gurbacewar muhalli da ta sauyin yanayi, tsohon babban sakataren MDD Kofi Annan ya yaba da yadda kasar Sin ta rubanya kokarinta ta fannin magance gurbacewar yanayi, da kyautata muhalli. Ya ce "A ganina, kasar Sin tana taka muhimmiyar rawa ta fannin sauyin yanayi da kuma muhalli, kuma ina da imanin cewa, gwamnatocin kasa da kasa za su yin koyi da ita."  (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China