in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar wakilan kasar Sin sun gabatar da taron jam'iyyar CPC a Habasha
2018-01-24 16:54:32 cri
A yau Laraba ne tawagar wakilan kasar Sin suka kammala ziyarar aiki ta kwanaki 3 a kasar Habasha, inda suka gabatar da nasarorin da babban taron jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin (CPC) karo na 19 ya cimma.

Bayan samun goron gayyata daga jam'iyyar (EPRDF) mai mulkin kasar Habasha, tawagar wakilan na kasar Sin karkashin jagorancin Wang Xiaohui, mataimakin shugaban sashen yada labarai na kwamitin tsakiya na jam'iyyar CPC, sun kai ziyarar aikin ne zuwa kasar ta gabashin Afrika tsakanin ranakun 22-24 ga watan Janairu. Wang, ya halarci taron tattaunawa wanda aka gudanar a kwalejin nazarin shugabanci ta Meles Zenawi da kuma jami'ar Addis Ababa, inda aka tattauna game da muhimman batutuwan da suka shafi babban taron na CPC karo 19.

Jam'iyyar ta EPRDF, ta nuna sha'awa matuka na kara karfafa yin hadin gwiwa ta kut-da-kut da CPC da kuma yin musayar kwarewa wajen tafiyar da sha'anin jam'iyyar da shugabancin kasar baki daya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China