in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Gambiya ya bukaci masanan kasar su yi koyi da kasar Sin
2018-01-24 12:39:20 cri
Jiya Talata, shugaban kasar Gambiya, Adama Barrow, ya bukaci masanan kasarsa su nuna himma da kwazo wajen gudanar da aiki, tare kuma da yin koyi da kasar Sin, ta yadda za'a raya tattalin arziki da kyautata zaman rayuwar al'ummar kasar, da kuma inganta ababen more rayuwar jama'a cikin sauri.

A cewar Adama Barrow, Gambiya na iya koyon nasarorin da kasar Sin ta samu ta fuskar bude kofa ga kasashen ketare. Ya ce, kasar Sin hamshakiyar kasa ce wadda ta iya samun babban ci gaba cikin shekaru kasa da arba'in, balle ma ita kasar Gambiya. Allah ya horewa Gambiya dimbin albarkatu, ciki har da girman kasa, da yankin da take a Afirka, da teku, wadanda dole ne Gambiya ta yi amfani da su.

Adama Barrow ya kara da cewa, bai kamata Gambiya ta gudanar da harkokinta kamar lokacin baya ba, idan har ta ci gaba da bin tsohuwar hanya ba za'a iya cimma burin raya wata sabuwar Gambiya ba.

Har wa yau, Adama Barrow ya shawarci jami'ansa da su nuna jaruntaka gami da zage damtse wajen samun nasara a fannin raya harkokin kasa.

A sau da dama shugaba Adama Barrow na Gambiya ya ambaci saurin bunkasar tattalin arzikin kasar Sin, musamman bayan da ya ziyarci birnin Beijing a watan Disambar bara.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China