in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Minista: Kamfani sarrafa fatu ginshiki ne na cigaban masana'antun Najeriya
2018-01-24 10:33:16 cri
Ministan kimiyya da fasaha na Najeriya ya bayyana cewa, masana'antun sarrafa fatu sun kasance jigo wajen raya masa'antun Najeriyar da samar da ayyukan yi da karuwar arziki.

Da yake jawabi a jahar Sokoto dake arewacin kasar, Ogbonnaya Onu, ya shedawa taron jama'a cewa, za'a iya samar da ayyukan yi sama da 700,000 daga masana'antun sarrafa fatun, ya kara da cewa, masana'antun sarrrafa fatun sun kasance a matsayin wani ginshiki na fadada hanyoyin tattalin arzikin kasar.

A cewar ministan, shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari yana aiki ba kakkautawa wajen inganta cigaban tattalin arziki da kyautata yanayin rayuwar jama'ar kasar ta hanyar karfafa masana'antun cikin gida da fadada hanyoyin tattalin arzikin kasar da kuma kawo sauye sauye a sha'anin tattalin arzikin.

A cewarsa, ma'aikatar zata karfafa gwiwa wajen shigar da 'yan kasar harkokin masana'antu da kuma amfani da fasahohin zamani.

Tun da farko, karamar ministar kasuwanci, masana'antu da zuba jari ta kasar Ai'sha Abubakar, ta shawarci 'yan Najeriya dasu rungumi hanyoyin samun bunkasuwar tattalin arziki ta hanyar kamfanonin sarrafa fatun, kana su bada fifiko wajen sha'awar sayen kayayyakin da aka sarrafa a cikin kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China