in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNRWA ya jaddada ci gaba da samar da tallafi ga 'yan gudun hijirar Palasdinu
2018-01-17 11:24:27 cri
Hukumar ba da agaji ga 'yan gudun hijirar Falasdinawa dake zaune a kasashen dake yammacin Asiya (UNRWA) a jiya Laraba ta bayar da sanarwar cewa, duk da barazanar da hukumar ke fuskanta daga kasar Amurka na daina samar mata kudin tallafi, amma hukumar za ta ci gaba da samar da tallafi ga 'yan gudun hijirar Palasdinu.

Kakakin hukumar Sami Mshasha, ya bayyana a cikin sanarwar cewa, "duk da matakan da aka dauka na tsuke bakin aljihu, amma hukumar za ta ci gaba da samar da tallafi ga 'yan gudun hijirar Palasdinu, kuma matakin da Amurka ta dauka na daina samar da taimakon kudi ga hukumar ba zai yi tasiri ga wannan alkawarin da hukumar ta dauka ba."

Kakakin ya ce, hukumar za ta dinga samar da tallafi ta fannonin rayuwa da agaji da kiwon lafiya da kuma ilmantarwa ga 'yan gudun hijirar Palasdinu kimanin miliyan 5.9 da suka yi rajista wadanda suka zo daga yamamcin gabar kogin Jordan da zirin Gaza da Syria da Lebanon da kuma Jordan. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China