in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Koriya ta kudu za ta tatttauna da Koriya ta arewa game da gasar wasannin Olympic na lokacin hunturu
2018-01-12 21:07:16 cri
Mahukuntan Koriya ta kudu sun yi tayin tattaunawa a mako mai zuwa da makwabciyarta koriya ta arewa a kauyen Panmunjom game da halartar tawagar koriya ta Arewa gasar wasannin Olympics na lokacin hunturu da Koriya ta kudu za ta karbi bakunci, kamar yadda ma'aikatar sassantawa kasar ta sanar a Jumma'ar nan

A ranar Talatar da ta gabata ce, manyan jami'an kasashen biyu suka tattauna a kauyen na Panmonjum, ganawa ta farko tsakanin sassan biyu cikin kimanin shekaru biyu, inda kasar Koriya ta Arewa ta amince ta tura tawaga zuwa gasar wasannin Olympics da ma na ajin na kasassu da zai gudana a watan Fabrairu zuwa watan Maris a garin Pyeongchang dake gabashin Koriya ta kudu.

A lokacin tattaunawar da ke tafe, batun halartar gasar da Koriya ta arewan za ta yi zai kasance cikin ajendar ganawar, kamar yadda 'yan wasa da jami'ai daga DPRK za su tsallaka kan iyaka zuwa Pyeongchang, da yawan mutanen da za su halarci gasar da kuma wurin da za su zauna.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China