in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin CPC: ba za a yiwa kundin tsarin mulki gyara sosai ba
2018-01-12 20:00:54 cri
Manyan shugabannin jam'iyyar kwaminis mai mulki ta kasar Sin(CPC) sun amince cewa, ya kamata gyaran da za a yiwa kundin tsarin mulkin kasar ya kunshi wasu sassa kadai a maimakon a yiwa kundin tsarin mulkin kasar gyara kwacakwan.

Mambobin hukumar siyasa na kwamitin koli na CPC sun jaddada cewa, kamata ya yi batun martaba shugabancin jam'iyyar da muradun jama'a su kasance ka'idar da za a bi wajen yiwa kundin tsarin mulkin kasar gyaran fuska.

Shugabannin sun saurari wani rahoto game da shawarwarin da aka tattara daga mambobin jam'iyya da wadanda ba sa cikin jam'iyya game da daftarin shawarar da kwamitin koli na jam'iyyar ya gabatar game da yiwa kundin tsarin mulkin kasar gyaran fuska

Daga bisani sun tattauna kan rahoton sannan suka yanke shawarar ci gaba da nazarin daftarin kamar yadda suka tattauna, sa'an nan za su gabatar da daftarin da aka yiwa gyaran fuska ga zama na biyu na kwamitin kolin jam'iyyar na 19 domin ya tantance.

A cewar shawarar da aka cimma yayin zaman, za a gudanar da zama na biyu na kwamitin koli na JKS na 19 daga ranar 18 zuwa 19 ga wannan wata.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China