in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi maraba da sakamakon tattaunawar Koriya ta Kudu da ta Arewa
2018-01-10 19:37:52 cri
Kasar Sin ta yi na'am da sakamakon tattaunawar da ta gudana tsakanin kasashen Koriya ta kudu da makwabciyarta ta Arewa.

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang wanda ya sanar da hakan Larabar nan yayin taron manema labarai da ya gudana a nan birnin Beijing ya ce, abin karfafa gwiwa ne yadda sassan biyu suka nuna kyakkyawan fata da rungumar juna a dai dai lokacin da yanayi a zirin Koriya ke kara tsananta.

Lu Kang ya ce, kasancewar kasar Sin wadda ke dab da zirin Koriya, ta yi maraba kana tana goyon bayan matakin da kasashen biyu suka dauka na kyautata alaka a tsakaninsu

Tattaunawa tsakani kasashen biyu wadda ita ce irinta ta farko cikin shekaru biyu, ta kai ga cimma yarjejeniya ciki har da yadda kasar Koriya ta arewa ta yarda ta tura tawaga zuwa gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu da za a gudanar a PyeongChang na kasar Koriya ta kudu da yin tattaunawar soja domin sassauta halin da ake ciki a zirin koriya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China