in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya tura babban sifeto 'yan sandan kasar zuwa jihar Benue sakamakon kashe-kashen da aka yi
2018-01-09 19:51:56 cri
Rahotanni daga Najeriya na cewa, shugaban kasar Muhammadu Buhari ya tura babban sifeton 'yan sandan kasar Ibrahim Idriss zuwa jihar Benue dake yankin arewa maso tsakiyar kasar, inda mutane sama da 50 suka rasa rayukansu a wasu hare-hare na baya-bayan da ake zargin Fulani da kaddamarwa.

Umarnin da shugaban ya bayar ya biyo bayan kiraye-kiraye da jama'a ke yi game da yanayin tsaro a jihar ta Benue.

Kakakin rundunar 'yan sandan Najeriya Jimoh Moshood, ya bayyana cewa, tuni aka tura Karin rukunonin 'yan sanda na musamman, da masu yaki da ta'addanci da 'yan sandan yau da kullum zuwa jihar kamar yadda shugaban ya ba da umarni.

Rahotanni na cewa, yanzu haka 'yan sanda sun yi nasarar kama mutane 8 da ake zargi da hannu a munanan hare-haren da aka kai a jihar.

A ranar 1 ga watan Nuwamban shekarar 2017 ne jihar ta Benue ta bullo da dokar hana kiwo a jihar. Dokar tana tanadi daurin shekaru biyar a gidan yari ga duk wanda ya karya ta.

Tun a farkon wannan shekarar ce kashe-kashe da ake zargin Fulani da aikatawa ke karuwa a al'ummomin Logo da Guma dake jihar ta Benue. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China