in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uganda ta karyata cimma yarjejeniya da Isra'ila game da karbar dubban 'yan gudun hirajar Afirka
2018-01-08 19:21:05 cri
Gwamnatin kasar Uganda ta karyata rahotanni dake cewa, wai ta cimma wata yarjejeniya da Isra'ila game da karbar dubban 'yan Afirka dake neman mafaka da aka baiwa wa'adin watanni uku su bar Isra'ila ko su fuskanci zaman gidan yari.

Karamin ministan harkokin kasa da kasa na kasar Uganda Henry Oryem Okello ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa,mahukuntan Uganda ba su cimma wata yarjejeniya da Isra'ila game da karbar masu neman mafaka sama da 35,000 galibinsu 'yan kasashen Eritrea da Sudan ba.

A makon da ya gabata ne dai mahukuntan Isra'ila suka baiwa 'yan Afirka dake neman mafaka da suka gujewa yaki da musgunawa wa'adin kwanaki 90 kan su bar kasar su koma kasarsu ta asali ko su nufi wata kasa ta dabam, ko kuma su fuskanci zaman gidan sarka, ba tare da bayyana sunan wata kasa ba.

Rahotanni na cewa, an baiwa 'yan gudun hijirar zabin ko dai su koma kasashensu na asali ko kuma a tusa keyarsu zuwa kasashen Uganda ko Rwanda.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China