in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Afrika zasu ci gajiyar zama mamba da AIIB
2018-01-07 13:26:43 cri
Wani masanin kasar Habasha yace kasashen Afrika zasu yi matukar cin moriyar zama mamba karkashin shirin bankin zuba jari don samar da ababen more rayuwa na Asiya wato (AIIB) a takaice.

Costantinos Bt. Costantinos, wanda jami'i ne mai bada shawara kan harkokin tattalin arziki na kungiyar tarayyar Afrika da hukumar gudanar da tattalin arzikin Afrika ta MDD, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, nan gaba kadan kasashen Afrika zasu bi sahun kasashen Afrika ta kudu, da Masar da Habasha wajen shiga shirin na AIIB.

Yace shirin wata babbar dama ce wanda zata samarwa kasashen cigaban ababen more rayuwa.

Costantinos, wanda kuma shehun malami ne a sashen nazarin dabarun jin dadin al'umma a jami'ar Addis Ababa yace, sakamakon zama mamba a shirin na hadin gwiwa da hukumomin samar da kudade wanda kasar Sin ta bullo dashi, a halin yanzu kasashen Habasha da sauran kasashen Afrika zasu iya samun damar karbar rancen kudade da samun tallafin ayyukan gina ababan more rayuwa.

A cewarsa, cigaban kayayyakin more rayuwa, da cigaban raya birane, da samar da gidaje, da masana'antu, da bunkasa aikin gona, da gina cigaban bil adama na daga cikin bangarorin da kasashen na Afrika zasu ci gajiya idan suka kasance mamba a AIIB.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China