in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Habasha za ta saki fursunonin siyasa dake tsare, a wani bangare na shirin afuwa
2018-01-04 10:46:27 cri
Kasar Habasha ta ce za ta saki 'yan adawa dake daure a gidan yari, a wani bangare na shirin afuwa domin samar da hadin kan kasa da inganta demokradiyya.

Cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin Facebook, Ofishin Firaministan kasar Hailemariam Desalegn ya ce za a rufe cibiyar tsare mutane na Maekalwi dake birnin Addis Ababa.

Sanarwa dai ba ta yi karin haske game da wadanda za a saki da kuma lokacin rufe cibiyar ba.

Magoya bayan bangaren adawa da masu zanga-zanga na zargin Gwamnatin kasar da amfani da cibiyar tsare mutanen wajen tilastawa wadanda ake zargi amsa laifi, inda ake tuhumarsu karkashin dokar da ta haramta ta'addanci.

Habasha ta fuskanci tashin hankali a shekarar 2016 da ya yi sanadin mutuwar daruruwan mutane, wanda masana suka bayyana a matsayin babban kalubalen da jam'iyyar kawance ta Ethiopian Peoples Revolutinary Democratic Front ta fuskanta cikin shekaru 25. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China