in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zambia ta sanar da matakan hana yaduwar cutar kwalara a gidajen yarin kasar
2018-01-04 09:29:57 cri
Gwamnatin kasar Zambia ta sanar da daukar kwararan matakai don tabbatar da cewa, cutar kwalara da ta barke a wasu sassan Lusaka, babban birnin kasar, ba ta bazu zuwa gidajen yarin kasar ba.

Ministan harkokin cikin gidan kasar Stephen Kampyongo wanda ya bayyana hakan a jiya Laraba, ya ce yanzu haka an dauki matakan da suka dace kamar yadda hukumomin lafiyar kasar suka tanada domin hana yaduwar cutar da ake dauka ta ruwa zuwa gidajen kurkukun kasar.

Ministan ya kuma shaidawa taron manema labarai cewa, daga yanzu hukumomin kula da gidajen yari ba za su bari a rika shigo da abinci daga waje zuwa cibiyoyin tsare jama'a ba. Haka kuma an haramta zirga-zirgar fursunoni da ma canzawa fursunoni wurin zama daga wannan gidan yari zuwa wancan.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China