in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jordan ta yi Allah wadai da harin da aka kai a wani masallaci a Najeriya
2018-01-04 09:22:36 cri
Ministan harkokin watsa labarai na kasar Jordan Mohammed Momani ya bayyana cewa, kasarsa ta yi Allah wadai da harin kunar bakin waken da aka kai kan wani masallaci dake garin Gamboru a yankin arewa maso gabashin Najeriya, harin da ya hallaka mutane 10.

Kamfanin dillancin labaran kasar ta Jordan Petra ya kuma ruwaito ministan na cewa, yadda kungiyoyin 'yan ta'adda ke kai hari kan masu Ibada da fararen hula, ya nuna munin akidunsu. A don haka ya ce, akwai bukatar a kara hada kai da daukar matakai don ganin bayan ayyukan ta'addanci. Ya kara da cewa, kasarsa tana goyon bayan matakan da mahukuntan Najeriyar ke dauka na yaki da 'yan ta'adda.

Wani matashi ne dai ya kutsa kai cikin wani masallaci a lokacin sallar Asubahin ranar Laraba, sannan ya tayar da abubuwan fashewar dake jikinsa. Baki daya dai mutane 10 ne aka tabbatar sun gamu da ajalinsu sanadiyyar harin, ciki har da mahaifin maharin. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China