in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ba ta da nufin zama jagora ko kuma maye gurbin wata kasa game da al'amuran duniya
2018-01-03 20:09:23 cri

A Larabar nan 3 ga wata ne kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya bayyana a yayin taron manema labaru cewa, kasar Sin na tinkarar al'amuran kasa da kasa bisa ka'idar yin shawarwari tare, da raya duniya tare, da cin moriyar bunkasuwar duniya tare. Kuma ko kadan ba ta da nufin yin jagoranci ko kuma maye gurbin wata kasa, yayin da ake tinkarar al'amuran duniya.

An labarta cewa, a kwanan baya, dandalin masana na kasar Amurka karkashin kamfanin Eurasia ya ce, a shekarar 2018, duniya za ta ci gaba da fuskantar koma-baya a fannin siyasa. Kuma kasar Sin tana yunkurin maye gurbin Amurka a wasu al'amuran duniya, wanda shi ne kalubale mafi tsanani a duniya a bana. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China