Sai dai kuma Mr. Kalaba ya ce zai ci gaba da zama mamba a majalisar dokokin kasar karkashin inuwar jam'iyya mai mulki. A ranar Litinin ne dai, Kalaba ya wallafa wata sanarwa a shafinsa na Facebook, inda ya bankado badakalar karuwar cin hanci a shekarar 2017, sanarwar da ta girgiza wasu 'yayan jam'iyyar,da har wasu ke kiran da ya yi murabus.
Koda yake kakakin shugaba Edgar Lungu na Zambia, Amos Chanda ya shaidawa kafofin watsa labaran kasar cewa, har yanzu fadar shugaban kasar ba ta karbi takardar yin murabus din tasa ba.
Mr Kalaba dai ya shafe sama da shekaru hudu yana rike da wannan mukami.(Ibrahim)