in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta bullo da yanayin kare muradun masu masana'antu bisa doka
2018-01-03 09:10:34 cri
Babbar kotun kolin al'umma ta kasar Sin ta bukaci daukacin kotuna dake fadin kasar da su samar da yanayin da ya dace ga masu masana'antu da kirkire-kirkire bisa doron doka

Wata takarda da kotun kolin ta fitar a jiya Talata, ta ce, an bukaci kotuna su yi amfani da matsayinsu wajen kare muradun masu masana'antu kamar yadda doka ta tanada, muddin masana'antun da kirkire-kirkiren wajen samar da kayayyaki da yadda suke tafiyar da harkokin kudi ba su saba dokoki ba.

Bugu da kari, sanarwar ta bukci kotunan da su bambance tsakanin kayayyakin da doka ta amince da ribar da ta sabawa doka da masana'antun ke samu.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa,wajibi ne kotunan su kare muradun halal na masana'antun, sannan su hukunta bata gari bisa tsarin doka. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China