Jiya Laraba ne, shugaban kasar Rasha Vladimir Putin, ya gabatar wa hukumar zaben kasar takardarsa ta neman sake tsayawa takara a zaben shugabancin kasar a matsayin dan takara mai zaman kansa. Rahotanni na cewa, hukumar zaben za ta kammala aikin tantance takardar Putin nan da kwanaki biyar masu zuwa.
A ranar 18 ga watan Maris din shekara ta 2018 ne za'a gudanar da zaben shugabancin Rasha. Kuma tun a ranar 18 ga watan da muke ciki ne aka fara yakin neman zaben a kasar. (Murtala Zhang)