in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sabon zababben shugaban ANC ya sha alwashin farfado da tattalin arzikin kasa
2017-12-25 10:44:43 cri
Sabon zababben shugaban jam'iyyar ANC mai mulki a Afirka ta kudu, kuma mataimakin shugaban kasar Cyril Ramaphosa, ya sha alwashin daukar matakan farfado da tattalin arzikin kasar.

Cikin sakon sa na bikin kirsimeti ga al'ummar kasar, Mr. Ramaphosa ya ce ya zama wajibi al'ummar kasar su yi aiki tare, wajen farfado da tattalin arzikin kasar ta hanyar kau da dukkanin shingaye, dake yiwa harkokin zuba jari tarnaki, tare da tabbatar da ci gaban kasar yadda ya kamata.

Ya ce duk da tarin irin ci gaba da aka samu a sassa daban daban a shekarar nan ta 2017, matsalolin karancin guraben ayyukan yi tsakanin al'ummar Afirka ta kudu na cikin matsaloli dake addabar kasar. Don haka ya yi kira ga al'ummar kasar, da su dukufa wajen ginin kasa ta hanyar marawa shirin samar da ci gaban kasar baya.

Mr. Ramaphosa ya kara da cewa, karkashin wannan tsari na bunkasa Afirka ta kudu, an tanaji matakai na samar da ci gaba a dukkanin sassa, da kyautata zamantakewar al'umma nan da shekarar 2030, yayin da kasar ke kara samar da dabarun cimma burikan ta na wadata, da biyan bukatun da suka shafi kwadago.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China