in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi maraba da yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya a Sudan ta Kudu
2017-12-22 19:42:14 cri
Kungiyar hadin kan Afirka ta AU, ta yi maraba da yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya da aka cimma tsakanin sassan dake adawa da juna a Sudan ta Kudu.

Da yake bayyana gamsuwa da hakan, shugaban hukumar zartaswar kungiyar Moussa Faki Mahamat, ya jinjinawa masu ruwa da tsaki game da cimma nasarar hakan.

Yarjejeniyar dai ta kunshi dakatar da kiyayya da juna, da kare rayukan fararen hula, tare da bada damar gabatar da kayayyakin jin kai ga masu bukata. An kuma sanya hannu kan ta ne yayin taron kungiyar raya gabashin Afirka ta IGAD, wanda aka bude a ranar 17 ga watan nan a birnin Addis Ababa na kasar Habasha.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China