in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojin saman Najeriya sun kaddamar da hare hare ta sama kan Boko Haram a jahar Borno
2017-12-17 13:31:40 cri
Rundunar sojojin sama ta Najeriya (NAF) ta fara lugudan wuta ta sama babu kakkautawa kan wasu maboyar 'yan ta'adda na Boko Haram a dajin Sambisa dake arewa maso gabashin kasar.

Mai magana da yawun hukumar ta NAF, Olatokunbo Adesanya, ya fada cikin wata sanarwa wadda aka baiwa kofenta ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Legas cewa, hare haren da sojojin kasar suka kaddamar kan maboyar ya hallaka 'yan ta'addan dake boye cikinsu.

A cewarsa, jiragen saman yakin sojin saman 4 ne suka yi ta lugudan wuta a yankunan da 'yan ta'addan suka mamaye.

Adesanya ya fada cikin sanarwar cewa, dakarun tabbatar da tsaro na "LAFIA DOLE" sun killace yankin da mayakan suke samun mafaka, inda suka yi ta barin wuta a yankin na Kolaram, mai tazarar kilomita 37 dake gabashin Monguno a jahar Borno

Yace, binciken sirri da dakarun tsaron kasar suka gudanar a lokutan baya ne ya gano yankin Kolaram wanda 'yan ta'adda na Boko Haram ke amfani dashi a matsayin mafaka, kuma daga can ne suke shirya kai hare haren ta'addanci a sansanonin sojin kasar dake arewacin jahar Borno.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China