in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IMF ya yaba wa masana'antun kasar Sin kan gudummawar da suka bayar a Habasha
2017-12-15 14:49:51 cri
Babbar darektar asusun ba da lamuni ta duniya (IMF) Christine Lagarde a jiya Alhamis, ta yaba wa masana'antun kasar Sin kan gudummawar da suka bayar wajen ci gaban kasar Habasha, bayan da ta kai ziyara yankin masana'antu na gabas dake kasar.

Babbar darektar ta bayyana cewa, masana'antun kasar Sin sun samar da dimbin guraben aikin yi a kasar Habasha, sun kuma kyautata kwarewar ma'aikatan wurin, abin da ya taimaka matuka ga samun dauwamammen ci gaban harkokin cinikayya da kasar ta Habasha ke yi da kasashen waje, da kuma sauyin tsarin tattalin arzikin kasar.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China