in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana goyon bayan kokarin da ake yi wajen warware batun zirin Koriya cikin ruwan sanyi ta hanyar tattaunawa
2017-12-12 20:57:25 cri

Yau Talata ne a nan Beijing, Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana cewa, kasar Sin tana amincewa da kuma goyon bayan kasashen Koriya ta Kudu da Koriya ta Arewa su kyautata huldarsu ta hanyar tattaunawa, kara azama kan samun sulhuntawa da yin hadin gwiwa, a kokarin taka rawa wajen sassauta tashin hanhali a zirin, kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a zirin.

A jiya ne madam Kyung-wha Kang, ministar harkokin wajen kasar Koriya ta Kudu ta ce, kamata ya yi a tuntubi Koriya ta Arewa kana a sanar da ita kiraye-kirayen da kasashen duniya suka yi mata, inda suka bukace da ta yi watsi da shirinta na nukiliya. Gwamnatin Koriya ta Kudu ta shirya tuntubar Koriya ta Arewa, a kokarin ganin ta kyautata hulda a tsakaninta da Koriya ta Arewa. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China