in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a bude taro zagaye na 8 game da sulhunta rikicin Syria
2017-12-12 12:18:52 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Kazakhstan ta bayyana cewa, za a bude taron shawarwari karo na 8 game da warware takaddamar siyasar kasar Syria a babban birnin kasar Astana. Za dai a gudanar da taron wanda Rasha ke jagoranta ne, tsakanin ranekun 21 zuwa 22 ga watan nan na Disamba.

Cikin sanarwar da ma'aikatar ta fitar ta shafin ta na yanar gizo, ta ce ana sa ran wakilai mahalarta taron za su tsara wani shiri, na samar da reshen da zai lura da sakin wadanda ake tsare da su, da mika gawawwakin wadanda suka rasu, tare da fara binciken wadanda suka bace.

Har ila yau yayin taron, za a tattuna game da hanyoyin dakile tashe tashen hankula a wasu sassan kasar ta Syria, tare da amincewa da sanawar da ta shafi bukatun jin kai a yankunan kasar da yaki ya daidaita.

Wannan taro dai na zuwa ne bayan wata ziyarar ba zata da shugaban Rasha Vladimir Putin ya kai kasar ta Syria a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa kasar sa, na daf da kwashe dakarun sojin ta daga Syria, bayan da aka cimma nasarar murkushe 'yan ta'adda a cikin kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China